in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
An kira taron kara wa juna sani kan hadin gwiwar samar da kayayyaki da makamashi tsakanin Sin da Afirka a Dar es Salaam
2016-07-06 10:49:50 cri
Jiya Litinin 5 ga wata, an kira taron karawa juna sani kan samar da kayayyaki da makamashi a tsakanin Sin da Afirka mai taken "damar da ake samu, kalubalolin da ake fuskanta da kuma shawarwarin da ake samar wa Afirka wajen raya masana'antu na zamani a nahiyar" a birnin Dar es Salaam na kasar Tanzania, wanda aka gudana bisa hadin gwiwar ofishin jakadancin kasar Sin dake kasar Tanzania da kuma ma'aikatar harkokin wajen kasar ta Tanzania.

A yayin bikin budewar taron, jakadan kasar Sin dake Tanzania Lu Youqing ya ce, kasar Sin tana son taimaka wa kasashen Afirka wajen raya harkokin tattalin arziki da zaman takewar al'umma ta hanyoyin samar musu fasahohin neman ci gaba da ta samu.

Haka kuma, ya ce, hadin gwiwar Sin da Tanzania na da makoma mai haske, bayan kasashen biyu suka kulla daftarin hadin gwiwar samar da kayayyaki da makamashi a watan Afrilu na shekarar 2015, sun yi ta tattaunawa kan yadda za a iya inganta hadin gwiwar kasashen biyu a wannan fanni, kuma sun cimma ra'ayi daya kan wasu batutuwan da abin ya shafa.

A nasa bangare kuma, ministan dake kula da harkokin gine-gine, sufuri da kuma sadarwa na kasar Tanzania Makame Mbarawa ya bayyana cewa, a halin yanzu, kasar Tanzania tana bukatar taimakon kudade, masana da kuma fasahohi matuka, lamarin da ya sa taimakon da kasar Sin ke samar wa kasarsa a wannan lokaci zai taimaka wa kasar Tanzania wajen gaggauta cimma burinta na kasancewar wata kasa mai samun kudin shiga na matsakaicin matsayi. (Maryam)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China