in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Ban Ki-moon ya kalubalanci gwamnatin Isra'ila da ta daina kafa sabbin matsugunan Yahudawa
2016-07-05 11:07:22 cri
A jiya Litinin 4 ga wata, ta bakin kakakinsa, babban sakataren MDD Ban Ki-moon ya ba da sanarwar yin Allah wadai da shawarar da Isra'ila ta yanke ta gina sabbin matsugunan Yahudawa a yammacin gabar kogin Jordan da gabashin birnin Kudus, kuma ya kalubalanci gwamnatin Isra'ila da ta dakatar da gina sabbin matsugunan.

Sanarwar ta ce, da babbar murya ce Ban Ki-moon ya yi Allah wadai da mahukuntan Isra'ila da suka dora niyyar gina sabbin gidajen kwana 560 a matsugunin Yahudawa a Ma'ale Adumim dake yammacin gabar kogin Jordan, da kuma wasu 240 a matsugunin Yahudawa a gabashin birnin Kudus.

Sanarwar ta ce, bangarorin hudu da batun Gabas ta Tsakiya ya shafa, wato MDD, da kungiyar EU, da Amurka, da kuma Rasha suka gabatar da wani rahoto domin yin kira ga Isra'ila da ta daina kafa matsugunan a kwanan baya, amma kuma abin takaici gwamnatin Isra'ila ta gabatar da wannan niyyarta. Game da hakan, Ban Ki-moon ya yi bakin ciki kwarai.

Ban Ki-moon ya nanata cewa, kafa matsugunan ya keta dokokin duniya. Ya kalubalanci gwamnatin Isra'ila da ta daina da kuma janye wannan niyya domin daddale yarjejeniyar karshe cikin zaman lafiya da adalci.(Fatima)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China