in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Gwamnatin Isra'ila za ta ci gaba da neman hanyoyin bunkasa zaman lafiya
2016-05-23 11:22:50 cri
Firaministan kasar Isra'ila Benjamin Netanyahu ya bayyana cewa, gwamnatinsa za ta ci gaba da daukar matakan wanzar da zaman lafiya tsakaninta da Falasdinawa ta hanyar diplomasiyya.

Netanyahu ya bayyana hakan ne yayin taron majalisar ministocin kasar, yana mai cewa gwamnatin hadakar kasar na ganin cewa ya zama dole a fadada majalisar ministocin kasar. Bayan gudanar da gyare-gyare ga gwamnatin, Isra'ila za ta ci gaba da dukufa ka'in da na'in wajen cimma burin samar da zaman lafiya ga al'ummar Falesdinu ta hanyar diplomasiyya a karkashin taimakon sauran kasashe.

A ranar 17 ga watan nan ne, shugaban kasar Masar Abdel Fattah Al-Sisi, ya bayyana cewa yanzu haka, akwai damar warware batun samar da zaman lafiya tsakanin Falesdinu da Isra'ila cikin ruwan sanyi, kuma kasar Masar na fatan taka rawar gani a shawarwarin, don cimma nasararsu, matakin da kuma Netanyahun ya yi maraba da shi.

A wata sabuwa kuma, a daren ranar Asabar, firaministan kasar Faransa Manuel Walls ya isa kasar Isra'ila, don fara ziyarar aiki ta yini uku a yankunan Falesdinu da Isra'ila. A kuma Litinin din nan Mr. Walls din zai yi shawarwari da Netanyahu, da shugaban Falesdinawa Mahmud Abbas, a wani mataki na karfafa shawarwari tsakanin Falesdinu da Isra'ila.(Bako)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China