in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Mutane 41 sun rasu sakamakon harin ta'addanci da aka kai a filin jirgin saman Turkiya
2016-06-30 11:08:31 cri
Ofishin gwamnan jihar Istanbul ta kasar Turkiyya ya fidda wata sanarwa a jiya Laraba cewa, harin kunar bakin waken da aka kai shekaran jiya Talata da dare a filin saukar jiragen sama na Ataturk ya yi sanadiyyar mutuwar mutane 41, a yayin da mutane 239 suka jikkata.

Haka kuma, sanarwar ta ce, cikin wadannan mutane 41 da suka rasu, akwai mutane 12 da suka zo daga ketare, ciki har da 'yan kasashen Saudiyya da Iran da Ukraine da sauransu.

Firaministan kasar Turkiya Bina Le Yıldırım ya bayyana a safiyar jiya Laraba cewa, akwai alamun da ke nuna cewa, kungiyar IS ce ta kai wannan hari, amma har yanzu, ana ci gaba da bincike don gano 'yan ta'addan da suka kai harin.

Gwamnatin kasar Turkiya ta kafa kwamitin musamman domin fuskantar harkokin gaggawa bayan aukuwar lamarin, rundunar 'yan sandan kasar ta kuma rufe filin saukar jiragen sama na Ataturk, da kuma dakatar da dukkan jiragen sama dake shiga ko fita daga filin. (Maryam)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China