in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
A kalla mutane 36 suka mutu sakamakon fashewar bom da aka samu a filin jiragen saman Istambul
2016-06-29 10:38:26 cri
Jiya Talata da dare, an samu jerin fashewar boma bomai na kunar bakin wake a filin jirgin saman Atatürk na Istambul, birnin da ya fi girma a kasar Turkiya, ya zuwa yanzu kimanin mutane 36 ne suka rasa rayukansu, sannan wasu sama da 140 suka ji rauni. Gwamnan lardin Istambul Vasip Sahin ya bayyana a filin jirgin saman cewa, fashewar bom din ya nuna cewar 'yan kunar bakin wake uku ne suka kai harin.

Firaministan kasar Turkiya Binali Yildirim ya bayar da sanarwa a safiyar yau Laraba cewa, kungiyar IS ce ta tayar da jerin boma-boman.

A jiya da dare shugaban kasar Turkiya Recep Tayyip Erdoğan ya bayar da sanarwa a rubuce, inda da babbar murya ya la'anci wannan harin na ta'addanci, ya kuma kalubalanci kasashen yamma da su dauki kwararan matakai wajen yaki da ta'addanci.

Sanarwar ta kuma nuna cewa, an kaddamar da wannan harin ta'addanci ne a watan azumi, wannan ya nuna cewa, 'yan ta'adda sun mayar da fararen hula a matsayin abubuwan da suka kai hari, da nufin lalata Turkiya ta hanyar zubar da jini.

A wannan rana kuma, babban sakataren MDD Ban Ki-Moon ya bayar da sanarwa ta bakin kakakinsa, inda ya la'anci harin ta'addanci da aka kai a filin jirgin saman na Atatürk, ya kuma jaddada cewa. Ya kamata kasashen duniya su kara kokari don yaki da ta'addanci. (Bilkisu)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China