Sanarwar ta bayyana cewa, sojojin saman Turkiya sun tura jiragen yaki 8 don kai harin kan dakarun PKK dake arewacin kasar Iraki, wanda ya taimaka wajen lalata wurare da dakunan ajiye makamai na mayakan PKK. Amma sanarwar ba ta bayyana yawan mutanen da suka mutu ko raunata a sakamakon harin ba.
A kwanakin baya, an sha fuskantar hare-haren ta'addanci a kasar Turkiya, lamarin da ya sanya gwamnatin kasar zafafa yakinta da dakarun PKK dake kudu maso gabashin kasar, tare da kama mutanen dake da alaka da kungiyar IS da sauran kungiyoyin masu tsattsauran ra'ayi a wurare daban daban na kasar, da kuma kara sa ido kan yankin iyakar kasa. (Zainab)