in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Nigeria ta fara bincike kan 'yan gudun hijira na tsawon kwanaki uku
2016-06-23 11:17:43 cri
A jiya Laraba 22 ga wata, gwamnatin Nigeria ta fara aikin yin bincike kan 'yan gudun hijira na tsawon kwanaki uku, kan wadanda suka yi gudun hijira daga kasar Niger zuwa garin Geidam na jihar Yobe dake arewa maso gabashin kasar sakamakon hare haren kungiyar Boko Haram.

Nahuta Abubakar, mai shiga tsakani na hukumar daidaita harkokin gaggawa ta Nigeria (NEMA) ya gaya wa wakilinmu cewa, 'yan gudun hijira sama da 5000 sun yi rajista, ciki har da yara 100 dake fama da karancin abincin gina jiki.

Wasu 'yan gudun hijira suna zama a wuraren da aka tsugunar da su, yayin da wasu suke zama a makarantu da hukumomi da sauransu.

Wadannan 'yan gudun hijira, wasu daga cikinsu sun zo daga Bosso da Diffa ta kasar Nijer, yayin da wasu suka zo daga jihohin Yobe da Borno na Nigeria.(Fatima)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China