in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Sojojin Najeriya na kara kaimi wajen yaki da 'yan ta'adda
2015-01-01 20:18:24 cri
Rundunar sojin Najeriya ta sake jaddada aniyarta ta daukar karin matakan dakile ayyukan kungiyoyin ta da kayar baya, da na 'yan ta'adda, a daukacin sassan kasar.

A cewar jami'in hulda da dama'a na rundunar Birgediya Janar Olajide Laleye, sabbin matakan da rundunar ke dauka a baya bayan nan, sun haifar da kyakkyawan sakamako, musamman a yankunan arewa maso gabashin kasar.

Laleye ya kara da cewa, za a baiwa daukacin jami'an da za su rika aiki a wannan yanki horo na musamman a fannin yaki da ayyukan ta'addanci kafin su fara aiki.

A wani ci gaban kuma, rundunar sojin dake ayyukanta a jihar Borno ta bayyana kafa dokar takaita zirga-zirgar ababen hawa ta kwanaki 2, a birnin Maiduguri, fadar gwamnatin jihar, dokar da za ta shafi kwanakin hutu na shagulgulan Maulidi da al'ummar musulmi ke gudanarwa a kowace shekara.

Tuni dai gwamnatin tarayyar Najeriyar ta ware ranekun Alhamis da Jumma'a a matsayin ranekun hutun bikin na Maulidi. (Saminu Hassan)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China