Jami'an tsaro a lardin Diffa da ke kudu maso gabashin jamhuriyar Nijar, sun tabbatar da mutuwar mutane a kalla 9 tare da wasu mutanen 13 da suka jikkata ciki hadda masu manyan raunuka, a wani hari da mayakan kungiyar Boko Haram suka kaddamar a garin Bosso.
Harin dai na jiya Laraba ya sanya dakarun sojojin gwamnatin kasar mayar da martani mai tsanani, inda suka samu nasarar harbe mayakan kungiyar har su 10.
A watan Febrairu na shekarar 2015 ne kasashen Najeriya, Kamaru, Nijar, Chadi da Benin, suka kafa wata rundunar hadin gwiwa mai sojoji 8700, a wani mataki na ganin bayan ayyukan mayakan na Boko Haram. (Tasallah Yuan)