in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Sojojin Nijer sun harbe dakarun Boko Haram guda 10
2016-05-29 12:56:03 cri
Jiya Asabar 28 ga wata, hukumar tsaron kasar Nijer ta sanar da cewa, sojojin gwamnatin kasar Nijer sun cimma nasarar yaki da dakarun kungiyar Boko Haram a yankin dake iyakar kudu maso gabashin kasar, inda suka harbe mayakan Boko Haram guda 10.

Dangane da wannan lamari, kakakin rundunar sojan kasar ya bayyana cewa, wasu mayakan Boko Haram sun kai hari ga wata tashar bincike ta soja dake garin Bosso na lardin Diffa, sa'an nan, sojojin kiyaye tsaron kasar sun mai da martani kan wadannan dakaru, inda suka hallaka mutane 10 daga cikinsu, sauran dakaru kuma suka gudu. A sa'i daya kuma, sojojin gwamnati guda uku sun jikkata.

Kaza lika, sojojin gwamnatin kasar Nijer suna ci gaba da neman sauran mayakan da suka kai hari da kuma suka tsere ta hanyoyin kasa da na sama.

Tun bayan kafuwarta a shekarar 2004, kungiyar Boko Haram ta janyo tashe-tashen hankula a yankin iyakar dake tsakanin kasar Nijeriya da Kamaru, haka kuma, bisa kididdigar da aka yi, an ce, tun shekarar 2009 ya zuwa yanzu, a kalla dakarun kungiyar sun kashe mutane dubu 15.

Haka kuma, a watan Fabrairu na shekarar 2015, kasashen Nijeriya, Kamaru, Nijer, Chadi da kuma Benin sun kafa wata rundunar soja mai kunshe da mutane 8700 cikin hadin gwiwa domin yaki da kungiyar Boko Haram. (Maryam)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China