in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Kasar Sin na mara wa MDD baya wajen tabbatar da kiyaye zaman lafiya cikin tsaro
2016-06-02 19:05:19 cri

Ranar 1 ga wata, zaunannen wakilin kasar Faransa a MDD Francois Delattre, wanda ke shugabantar kwamitin sulhu na MDD a wannan wata ya ce, mambobin kwamitin za su tattauna kan kyautata injuna mallakar rundunar wanzar da kwanciyar hankali ta MDD a kasar Mali da kuma kwarewar sojojin rundunar ta gudanar da aikinsu a wannan wata.

Dangane da lamarin, madam Hua Chunying, kakakin ma'aikatar harkokin wajen kasar Sin ta bayyana yau 2 ga wata a nan Beijing cewa, kasar Sin ta yi tir da harin ta'addanci da aka kai wa rundunar wanzar da kwanciyar hankali ta MDD a kasar Mali a ranar 31 ga watan jiya. Kasar Sin na mara wa kwamitin sulhu na MDD baya wajen yin tattaunawa kan yadda za a inganta aikin tsaro yayin da sojojin kiyaye zaman lafiya na MDD suke gudanar da aikinsu. (Tasallah Yuan)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China