in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Kakakin ma'aikatar harkokin wajen Sin ta yi bayani kan rasuwar ma'aikacin wanzar da zaman lafiya na Sin a Mali
2016-06-01 19:24:28 cri
Mai magana da yawun ma'aikatar harkokin wajen kasar Sin Hua Chunying, ta yi bayani kan rasuwar ma'aikacin kiyaye zaman lafiya da kasar Sin ta tura zuwa kasar Mali.

Hua Chunying ta bayyana hakan ne a yau Laraba 1 ga watan Yuni, inda ta ce, an kaiwa tawagar jami'an wanzar da zaman lafiya hari a sansanin tawagar ta MDD dake kasar Mali, lamarin da ya haddasa rasuwar mutane da dama, cikin har da sojan kasar Sin guda daya, yayin da sojojin Sin guda hudu suka jikkata.

A cewarta, wannan al'amari ya bata ran kasar Sin, kuma gwamnatin na nuna matukar juyayi, tare da jajantawa iyalan sojan na Sin da ya rasu, da kuma jajantawa 'yan uwan sojojin da suka jikkata.

Bugu da kari, Hua Chunying ta jaddada cewa, kasar Sin tana tsayawa tsayin daka wajen goyon bayan aikin kiyaye zaman lafiya na kasa da kasa, za ta kuma ci gaba da goyon bayan aiki kiyaye zaman lafiya, da zaman karko a nahiyar Afirka. (Maryam)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China