Wata sanarwa da tawagar wanzar da zaman lafiya ta MDD da ke Mali ta fitar, ta bayyana cewa, tawagar ta kasar Sin mai ma'aikata 395 da aka tura kasar ta Mali, tana kan hanyarta ta dawowa gida kasar Sin, bayan da suka kammala aikinsu na shimfida zaman lafiya a kasar cikin nasara.
Tuni tawaga ta hudu da ke gudanar da irin wannan aiki ta maye gurbinta.(Ibrahim)