in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
AU ta yi Allah wadai da hare-haren da ake ta kaiwa a Mali
2016-06-01 10:06:32 cri
Kungiyar tarayyar Afirka wato AU ta yi Allah-wadai da kakkausar murya kan hare-haren da aka sake kaiwa dakarun kasar Mali da na tawagar kasa da kasa da ke aikin wanzar da zaman lafiya a kasar.

Wata sanarwa da shugabar hukumar zartarwar kungiyar Nkosazana Dlamini Zuma ta rabawa manema labarai, ta yi Allah-wadai da hare-haren da aka sake kaiwa dakarun gwamnatin Malin a yankin Ansongo da kuma wanda aka kaiwa sojojin kasar Togo da ke aiki a tawagar MINUSMA a kasar ta Mali, hare-haren da suka haddasa mutuwar sojoji da dama kana wasu da dama suka jikkata.

A cewar sanarwar, Madam Zuma ta kara bayyana damuwa kan yadda ake yawaita kai hare-hare a yankin arewacin Mali da sauran kasashen da ke shiyyar.

Sai dai Uwar gida Zuma ta bayyana kudurin kungiyar AU na nuna goyon baya ga Mali da tawagar MINUSMA, musamman gwamnatin Togo da mutanen da wannan lamarin ya shafa.

Ta kuma yi amfani da wannan dama wajen mika sakon ta'aziyar kungiyar ta AU ga iyalan wadanda suka rasa 'yan uwansu,tare da fatan samun sauki cikin hanzari ga wadanda suka jikkata.

Madam Zuma ta kuma yaba rawar da dakarun ke takawa a yankin.(Ibrahim)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China