Wata sanarwar da ma'aikatar tsaron kasar Mali ta gabatar a jiya Jumma'a 27 ga wata, ta ce, wadannan motoci guda 2 suna wajen kan iyakar yankin Gao da yankin Menaka ne duk a arewacin kasar Mali, lokacin da suka gamu da harin fashewar wata nakiya. Dukkan mutanen da suka rasa rayuka da jin raunuka sakamakon harin nan sojoji ne dake cikin motocin 2.
A cikin sanarwar, ma'aikatar tsaron kasar Mali ta ce gwamnatin kasar za ta yi iyakacin kokarinta don gurfanar da wadanda suka kai wannan harin gaban kotu.
Sai dai har zuwa yanzu, babu wata kungiya ko wani mutum da ya yi ikirarin daukar alhakin wannan hari. (Bello Wang)