in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
MDD ta yi Allah wadai da harin da aka kai kan ma'aikatan kiyaye zaman lafiya a Mali
2016-05-30 13:30:55 cri
A jiya Lahadi ne, babban sakataren MDD Ban Ki-moon da kwamitin sulhun MDD suka ba da sanarwa daya bayan daya, inda suka yi Allah wadai da harin da aka kai kan ma'aikatan kiyaye zaman lafiya a Mali, tare da kalubalantar gwamnatin Mali da ta gaggauta gudanar da bincike kan lamarin.

Jiya rana ce ta ma'aikatan kiyaye zaman lafiya ta duniya. A wannan rana, ta bakin kakakinsa, Ban Ki-moon ya ba da sanarwar cewa, an aikata wannan danyen aiki a wannan ranar da kamata a girmama jaruntaka da sadaukar da rai da ma'aikatan kiyaye zaman lafiya na MDD suka nuna, lallai wannan abin bakin ciki ne kwarai.

Bisa dokokin kasa da kasa, irin wannan harin da aka kaddamar tamkar laifin yaki ne. Don haka ya yi kira da a hanzarta cafke wadanda suka kai wannan harin.

Bugu da kari, a wannan rana, kwamitin sulhun MDD ya ba da wata sanarwar yin allah-wadai da babbar murya kan wannan hari, kana ya kalubalanci gwamnatin Mali da ta hanzarta gudanar da bincike kan harin.(Fatima)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China