in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Sojojin Najeriya sun cimma gagarumar nasara a yakin da suke yi da 'yan Boko Haram
2016-05-10 11:06:17 cri
Kakakin rundunar sojojin Najeriya Kanar Sani Usman, ya ce sojojin kasar dake yaki da kungiyar Boko Haram a arewa maso gabashin Najeriya sun cimma manyan nasarori a ayyukan da suke gudanarwa, musamman ma a dajin Sambisa, wanda ya zamo tungar 'yan Boko Haram ta karshe.

Cikin wata sanarwa da ya fitar, kanar Usman ya ce cikin kwanaki 12 sojojin sun fatattaki mayakan kungiyar a sansanonin su dake sassan wannan daji. A cewar sa dakarun tawagar ta 7 dake karkashin runduna ta 21 ta sojin kasar, sun hallaka 'yan ta'adda da dama, sun kuma kori 'yan kungiyar daga kauyuka 4 da kuma wasu wuraren da suke samun mafaka a yankunan Bala Karege, da Goske, da Harda da kuma Markas 3.

Sanarwar ta kara da cewa ya zuwa ranar Lahadi 8 ga watan Mayun nan, sojojin sun shiga wadannan sassa, inda a wurare da dama 'yan Boko Haram din sun riga sun arce kafin shigar sojojin.

Kaza lika sanarwar ta ce dakarun sojin sun gano makamai da sauran kayan fada da mayakan na Boko Haram ke amfani da su. Har wa yau a cewar kanar Usman, mayakan kungiyar sun yi amfani da ruwan sama mai karfi da aka tashi da shi a ranar Lahadi, wajen matsawa sansanin sojojin Najeriyar dake dajin na Sambisa. (Saminu)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China