in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Kasar Sin tana maraba da ci gaban da aka samu a yunkurin shimfida zaman lafiya a kasar Sudan ta Kudu
2016-02-15 18:55:09 cri
Sin ta bayyana cewa, tana maraba da ci gaban da aka sama a yunkurin da ake yi na shimfida zaman lafiya a kasar Sudan ta Kudu. kakakin ma'aikatar harkokin waje ta Sin, Hong Lei wanda ya bayyana hakan yau a gun taron manema labaru ya kuma ce, kasar Sin tana fatan ci gaba da taka rawar a zo a gani a kokarin tabbatar da zaman lafiya da kwanciyar hankali da kuma bunkasuwa a kasar Sudan ta Kudu.

Rahotanni na cewa, a ranar Asabar din da ta gabata ce, jagoran bangaren da ke adawa da gwamnatin Sudan ta Kudu, Riek Machar ya bayyana amincewa da nadin da shugaba Salva Kiir Mayardit ya yi masa na zama mataimakinsa na farko.

Game da wannan batu, Hong Lei ya ce, Sin tana maraba da ci gaban da aka samu a kokarin da ake yi na shimfida zaman lafiya a kasar Sudan ta Kudu. Tana kuma fatan za a hanzarta kafa gwamnatin hadaka da za ta kunshi dukkan al'ummomi, domin sa kaimi ga wannan yunkuri. Sin za ta ci gaba da ba da gudummawa tare da sauran kasashe da kungiyoyin duniya da abin ya shafa, domin sa kaimi ga tabbatar da zaman lafiya da kwanciyar hankali da bunkasuwa a kasar yadda ya kamata.(Fatima)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China