in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Afirka ta Kudu na shawarta ficewa daga kotun ICC
2016-02-05 08:54:59 cri
Ministar ma'aikatar huldar kasashen wajen kasar Afirka ta Kudu Mait Nkoana-Mashabane, ta bayyana yiwuwar ficewar kasar ta daga kotun hukunta manyan laifuka ta kasa da kasa ko ICC a takaice.

Hakan dai ya biyo bayan zargin da aka dade ana yi, cewa kotun na nunawa nahiyar Afirka banbanci cikin ayyukan ta, matakin da ya sabawa manufar kafa ta. Ministar wadda ta bayyana hakan a ranar Alhamis, yayin wani taron manema labarai a birnin Pretoria, ta kara da cewa kasar ta, zata tattauna da daukacin masu ruwa da tsaki, tare da ita kanta kotun ta ICC, domin kara nazartar yanayin da ake ciki, kafin kaiwa ga daukar matakin karshe.

Kalaman na Nkoana-Mashabane dai tamkar jaddada ra'ayin da shugaba Jacob Zuma ya gabatar ne, yayin taron kungiyar AU da ya gabata a 'yan kwanaki, inda ya bayyana rashin gamsuwar kasar sa ga ayyukan ICCn, tare da bayyana yiwuwar janyewa daga goya mata baya.(Saminu Alhassan)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China