in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
An yi kira da a kara samar da taimakon kudi domin ilimantar da yara 'yan gudun hijira
2016-05-24 10:33:24 cri
Jiya Litinin, mataimakin shugaban kwamitin tattalin arziki da zaman takewar al'umma na MDD Sven Jurgenson, ya yi kira ga gamayyar kasa da kasa, da su maida hankali kan samar da damar neman ilimi ga yara, wadanda suke fama da matsalolin jin kai. Mr. Jurgenson ya kuma yi kira da a kara samar da taimakon kudin, wadanda za a yi amfani da su wajen ba da ilmi ga yara 'yan gudun hijira.

Mr. Jurgenson ya bayyana haka ne, a yayin taron kolin jin kai na kasa da kasa karo na farko da aka bude a birnin Istanbul na kasar Turkiya a wannan rana. Haka kuma, a yayin taron kolin, an kira wani taro mai taken "kare ko wane yaro da ko wace yarinya, neman ci gaba yayin da ake kiyaye yanayin jin kai yadda ya kamata".

Bugu da kari, babbar sakatariyar hukumar kyautata ilmi, kimiyya da al'ada ta MDD wato UNESCO Irina Bokova, ta yi fatan cewa, gamayyar kasa da kasa za su iya kara yawan taimakon kudi da suke baiwa MDD, domin kyautata ayyukan koyar da yara.

Kaza lika, bisa kididdigar da aka yi, an ce, a halin yanzu, adadin yaran da ba sa iya zuwa makarantu a duniya ya kai miliyan 123, kuma yara kimanin miliyan 168 suna aikin karfi domin karancin kudi. Har wa yau adadin yaran da ake sayar da su ya kai kimanin miliyan 1.2 a ko wace shekara. (Maryam)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China