in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Wakilan kasashe 173 za su tattauna batun kare muhallin duniya a Nairobi
2016-05-19 10:27:41 cri
Shugaban hukumar kare muhalli ta MDD Achim Steiner ya bayyana a jiya Laraba cewa, za a kira babban taron kare muhallin duniya na MDD karo na biyu a babban birnin kasar Kenya, Nairobi daga ranar 23 zuwa ranar 27 ga wata, inda wakilai daga kasashe guda 173 za su hallara a birnin Nairobi domin tattauna batun kare muhallin duniya tare.

A yayin taron manema labarai da aka yi a wannan rana, Mr. Steiner ya yi bayani kan wasu abubuwan da suka shafi babban taron da za a yi a birnin Nairobi. Ya ce, mahalartar taron za su tattauna batutuwan da suka shafi yadda ake fitar da gurbatacciyar iska, cinikin namun daji ba bisa doka ba, kare muhallin teku, tarin sharar kayan abinci, sharar masana'antu da dai sauransu.

A sa'i daya kuma, wakilan za su yi shawarwari kan yadda za a aiwatar da yarjejeniyar Paris da aka cimma a karshen shekarar da ta gabata, da kuma neman dauwamammen ci gaban duniya. Haka kuma, ministocin dake kula da harkokin kiyaye muhalli sama da dari daya na kasashen duniya za su halarci tattaunawar da za a yi.

Taken taron na wannan karo shi ne" cimma burinmu na samun dauwamammen ci gaba a fannin kare muhalli bisa jadawalin samun dauwamammen ci gaba a shekarar 2030".Ana kuma sa ran za a tattauna sabbin batutuwan kare muhalli a yankuna da kuma a kasashe daban daban na duniya. Daga bisani kuma, za a zartas da wasu kudurorin da abin ya shafa, ta yadda al'ummomin kasa da kasa za su samu zarafin fuskantar kalubalolin da abin ya shafa cikin hadin gwiwa. (Maryam)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China