in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Kasar Sin shirin bunkasa makamashin nukiliya mai tsafta
2015-12-23 20:29:16 cri
Kasar Sin ta bayyana shirinta na kara bunkasa makamashin nukiliya a kokarin da take na kara yawan makamashi maras gurbata muhalli da ta ke fatan amfani da shi na kashi 20 cikin 100 ya zuwa shekara 2030.

Wakilin musamman na kasar Sin a taron sauyin yanayi na MDD da ya gudana a birnin Paris na kasar Faransa Xie Zhenhua ne ya bayyana hakan yayin taron manema labarai da majalisar gudanarwa ta kasar Sin ta shirya yau a nan birnin Beijing.

Mr Xie ya ce, ana gina tashohin nukiliya a wasu wurare da suka dace da ke bakin teku kana ana daga matsayin na'urorin da ke wurin.

Bugu da kari, kasar Sin za ta zabi wasu wurare a babban yankin kasar domin gina tashoshin makamashin nukiliya, amma har yanzu ana tattaunawa game da wuraren da suka dace a gina wadannan tashoshi.

Jami'in ya ce, batun tsaro na daga cikin muhimman batutuwan da ya kamata a yi la'akari da su wajen gina wadannan tashoshi shi ne tsaro, don haka kasar Sin ta himmatu wajen tabbatar da samar da na'urori, da kuma wurin da ya dace. (Ibrahim)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China