in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Kasar Sin ta kasance ta 85 a jerin sunayen kasashe masu ingancin muhalli
2016-02-26 10:02:09 cri
An fitar da takardar bayani game da jerin kasashe masu ingancin muhalli a birnin Beijing na kasar Sin a ranar Alhamis, inda bisa kididigar da aka gudanar a shekarar 2014, kasar Sin ta kasance ta 85 a duniya, matsayin da ya daga kadan sama da na 87 da ta samu a shekarar 2012.

Masu wallafa takardar bayanin sun hada da masanan jami'ar horar da malamai ta lardin Fujian na kasar Sin, da na cibiyar nazarin fasahar tsara muhalli ta ma'aikatar kare muhallin kasar, da na mujallar kula da duniya ta cibiyar nazarin fasahar samun ci gaba ta majalisar gudanarwar kasar, da dai makamantansu. Wadannan sassa sun yi nazari ne kan yanayin da kasashe 133 suke ciki a kokarin kare muhalli.

Takardar ta sheda cewa, cikin kasashe 30 dake kan gaba a jerin sunayen, 17 daga cikin su kasashe ne masu sukuni, yayin da kuma kusan dukkan kasashen dake koma baya a wannan fanni kasashe ne da tattalin arzikinsu ke tasowa. Dalilin da ya sa haka a cewar takardar, shi ne an dade ana samun babban gibi tsakanin kasashe masu sukuni da kasashe masu tasowa, musamman a fannonin ci gaban tattalin arziki, da yawan kudin da ake zubawa a fannin kare muhalli, da tsarin gudanar da aikin kare muhalli, da ingancin fasahar daidaita muhalli, da dai makamantansu.

Sa'an nan, idan an kwatanta yanayin da ake ciki a nahiyoyi 6 na duniya, za a ga cewa nahiyar Oceania ta fi ci gaba ta fuskar samun ingancin muhalli a shekarar 2014, yayin da nahiyar Afirka ta fi koma baya, a cewar takardar bayanin. (Bello Wang)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China