in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Ministan harkokin waje na Sin ya gana da takwaransa na Sudan
2016-05-13 10:57:37 cri
A jiya Alhamis 12 ga wata, ministan harkokin waje na Sin Wang Yi ya gana da takwaransa na Sudan, Ibrahim Ghandour, bayan halartar taron ministoci karo na 7 na dandalin tattaunawar hadin gwiwa tsakanin Sin da kasashen Larabawa a birnin Doha.

A yayin ganawarsu, minista Ghandour ya nuna godiya ga kasar Sin wajen ba da gudummawa ga cimma nasarar dandalin tattaunawar, ya yi imani da cewa, dandalin zai sa kaimi ga dangantaka tsakanin kasashen Larabawa da Sin zuwa wani sabon mataki. Ya kara da cewa, Sudan tana nuna goyon baya ga matsayin da Sin ke dauka kan batun tekun kudancinta, tana nuna goyon baya ga kokarin da Sin ke yi na kiyaye cikakken yankin kasa da iko da moriyarta bisa dokoki. Dadin dadawa, minista Ghandour ya gabatar da yanayin da ake ciki a Sudan da kuma yunkurin tabbatar da zaman lafiya a kasar, ya ce, Sudan tana godiya ga kasar Sin wajen nuna goyon baya ga yunkurin tabbatar da zaman lafiya a kasar da taimakawa bunkasa tattalin arzikinta. Da fatan Sin za ta ci gaba da nuna mata goyon baya kamar yadda ta saba.

A nasa bangare, minista Wang Yi ya bayyana cewa, Sin za ta tsaya tsayin daka kan nuna goyon baya ga kasar Sudan wajen samun moriyarta bisa dokoki kan batun Darfur da sauransu, kuma za ta ci gaba da sa kaimi ga kamfanonin Sin da su gudanar da harkokinsu a Sudan. Da fatan Sudan za ta yi amfani da dandalin tattaunawar hadin gwiwa tsakanin Sin da kasashen Afirka, da dandalin tattaunawar hadin gwiwa tsakanin Sin da kasashen Larabawa, domin karfafa hadin gwiwarta da Sin yadda ya kamata.(Fatima)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China