A jiya Talata ne, Li Lianhe, jakadan kasar Sin da ke kasar Sudan ya rubuta wani sharhi cikin wata shararriyar jaridar kasar Sudan, inda ya bayyana cewar, zumunci mai karfi da ke tsakanin kasashen Sin da Larabawa da kuma hadin gwiwarsu, za su kyautata huldar abokantaka da ke tsakanin kasashen Sin da Sudan bisa manyan tsare-tsare. (Tasallah Yuan)