in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Sin ba za ta amince da hukuncin da za a yanke kan karar Tekun Kudu ba
2016-05-08 13:20:31 cri
A ran 6 ga wata, shugaban sashen kula da harkokin kan iyakokin kasa da kasa da yankunan teku na kasar Sin na ma'aikatar harkokin wajen kasar Ouyang Yujing ya yi bayani kan dalilin da ya sa kasar Sin ba za ta amince da kuma halarci hukuncin da za a yanke kan karar Tekun Kudu da kasar Philippines ta gabatar ba.

Cikin bayanin da ya yi, Mr. Ouyang ya ce, anihin batun Tekun Kudu shi ne batun mallakar wasu kanannan tsibirai a yankin kasar Sin da kasar Philippines ta yi ba bisa doka ba, da kuma wasu matsalolin dake shafar yanke iyakar teku bisa kafuwar sabuwar tsarin dokar teku.

Sa'an nan, Mr. Ouyang ya kara da cewa, yarjejeniyar dokar teku ta MDD ba ta shafi ikon mallakar yankin teku ba, shi ya sa, kasar Sin ta riga ta sanar da cewa, ba ta amince da wannan yarjejeniya a kan batun yanke iyakar teku ba, shi ya sa, kasar Sin ta ba da sanarwar cewar ba ta amince da kuma halartar hukuncin da za a yanke kan karar Tekun Kudu da kasar Philippines ta gabatar ba, wannan matakin da kasar Sin ta dauka ya dace da yarjejeniyar da sauran dokokin kasa da kasa. Sabo da an yanke wannan hukunci ba bisa doka ba, shi ya sa, kasar Sin ba za ta amince da kuma karbar sakamakon da za a fidda game da wannan kara ba. (Maryam)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China