in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Ma'aikatan samar da agaji da Sin ta tura zuwa Philippines sun ceci mutane sama da dubu daya
2013-11-28 16:20:45 cri

Kakakin ma'aikatar harkokin wajen kasar Sin Qin Gang ya bayyana cewa, ma'aikatan samar da agaji da kasar Sin ta tura zuwa kasar Philippines sun azama wajen gudanar da ayyukansu na ceto wannan kasa, kuma ya zuwa yanzu, sun riga sun ceto mutane sama da dubu daya.

Yayin taron manema labaran da aka yi a ranar 27 ga wata, Qin Gang ya bayyana cewa, ma'aikatan samar da agaji da kasar Sin ta tura zuwa kasar Philippines dake kunshe da masu samar da agajin gaggawa, likitoci da kuma jirgin ruwan bada jinya sun dukufa wajen gudanar da ayyukansu tun isarsu kasar Philippines, inda suka ceto mutane sama da dubu daya, da kuma gano gawawwaki guda 22. Mr. Qin ya bayyana cewa, ma'aikatan za su ci gaba da gudanar da ayyukansu yadda ya kamata, kuma gwamnatin kasar Philippines ta bayyana matukar godiya bisa ga taimakon da ma'aikatan kasar Sin suka bayar a wannan kasa. (Maryam)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China