in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
MDD ta bukaci bangarorin da rikicin Syria ya shafa da su tsagaita bude wuta a Aleppo
2016-05-05 10:16:40 cri

Jiya Laraba, mataimakin babban magatakardan MDD mai kula da harkokin siyasa Jeffrey Feltman ya yi kira ga bangarori daban daban da rikicin kasar Syria ya shafa da su tsagaita musayar wuta a tsakanin su a birnin Aleppo dake arewacin kasar ba tare da bata lokaci ba.

A wannan rana, kwamitin sulhu na MDD ya kira wani taron gaggawa kan yanayin da birnin Aleppo ke ciki a halin yanzu, inda Mr. Feltman ya ce, ya kamata a warware rikicin Syria ta hanyar siyasa, haka kuma, MDD na son ba da taimako yadda ya kamata domin farfado da shawarwarin neman sulhu a Syria cikin hanzari.

A nasa bangaren, mataimakin babban magatakardan MDD mai kula da harkokin jin kai Stephen O'Brien ya bayyana a yayin taron cewa, al'ummomin dake birnin Aleppo suna ci gaba da fuskantar tabarbarewar yanayin zaman rayuwarsu, shi ya sa, yake sa kaimi ga bangarori daban daban da abin ya shafa da su bi dokokin kasa da kasa yadda ya kamata, da kuma ba da taimako gare su ta hanyoyin da suka dace. (Maryam)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China