in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
An kai harin ta'addanci kan karamin ofishin jakadancin Rasha a Syria
2016-04-30 13:01:17 cri
A jiya Jumma'a tashar yanar gizo ta ma'aikatar harkokin wajen Rasha ta ba da labarin cewa, a ranar Alhamis da ta gabata ne, kungiyar ta'addanci ta "Al-Nusra Front" ta kaddamar da harin luguden wuta kan karamin ofishin jakadancin Rasha dake birnin Aleppo na kasar Syria, kuma ma'aikatar ta yi Allah wadai da wannan danyen aiki da babbar murya.

Da ma dai sakamakon matsalar tabarbarewar tsaro a kasar, ofishin jakadancin ya daina aiki tun a watan Janairun shekarar 2013, yayin da aka tura wasu ma'aikatan ofishin zuwa birnin Damascus, hedkwatar kasar. Kawo yanzu dai, wasu ma'aikata 'yan Syria ne kadai ke cigaba da gudanar da aikinsu a ofishin.

A jiya Juma'a, kamfanin dillancin labaru na Syria ya ba da labarin cewa, birnin Aleppo dake arewacin kasar ya sake fuskantar luguden wuta. Wannan ne rana ta 7 a jere, da ake kaddamar da hari a birnin, wanda ya yi sanadiyyar mutuwar mutane sama da 100.

A ranar 28 ga wata, yayin da ministan watsa labaru na Syria, Omran Zoabi ya yi magana da wakilin gidan talebijin din kasar, ya bayyana cewa, jerin hare haren da ake kaiwa birnin Aleppo a kwanan baya tamkanr laifin yaki ne, wanda a cewarsa, ya zama dole gwamnatin Syria da sojoji su mai da martani.

Birnin Aleppo ya taba zama cibiyar tattalin arzikin kasar Syria, kuma birni mafi girma a kasar. Yanzu sojojin kasar da dakaru masu adawa da gwamnatin kasar da kuma kungiyoyin masu tsattsauran ra'ayi sun mamaye wurare daban daban na wannan birni.(Fatima)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China