in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Syria: Harin roka a Aleppo ya haddasa mutuwar mutane 25
2016-05-01 12:55:30 cri
Kamfanin dillancin labaru na kasar Syria ya ba da labarin a ranar 30 ga watan Afrilu cewa, cikin sa'o'i 24 da suka wuce, an kai hare-haren rokoki a birnin Aleppo dake arewacin kasar, lamarin da ya yi sanadiyyar mutuwar fararen hula 25, tare da raunatar wasu fiye da 80.

An bayyana cewar, reshen kungiyar al-Qaida dake kasar Syria na Al-Nusra ya kai hare-haren kan wasu ungwannin fararen hulda dake birnin Aleppo, wadanda suka fara daga ranar 29 har zuwa ranar 30 ga wata.

Bayan da kasashen Amurka da Rasha suka cimma yarjejeniya don ganin bangarorin da ba sa ga maciji da juna a kasar Syria su tsagaita bude wuta a ranar 22 ga watan Fabrairun bana, an samu sassauci game da yanayin tsaro a wannan kasar. Sai dai a 'yan kwanakin baya, yanayin kasar ya sake tsanantawa, sakamakon janye jiki na wasu kungiyoyin masu adawa da gwamnati daga cikin yarjejeniyar.(Bello Wang)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China