in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
An kira taron ministocin harkokin waje karo na 5 na CICA a birnin Beijing
2016-04-28 20:14:25 cri
A yau Alhamis ne aka gudanar da taron ministocin harkokin waje na taron musayar ra'ayoyi da inganta amincewa da juna na nahiyar Asiya wato CICA karo na biyar a birnin Beijing, inda ministocin harkokin waje na taron na CICA, da na kasashe masu sa ido, da shugabannin kungiyoyin shiyya shiyya da na duniya kimanin 40 suka halarci wannan taro.

Ministan harkokin waje na Sin Wang Yi wanda ya jagoranci taron ya kuma gabatar da jawabi.

Wang Yi ya ce, tun bayan da ya hau kujerar shugabancin taron CICA a shekarar 2014, Sin tana martaba ra'ayin tsaro na yankin Asiya tare da yin hadin gwiwa tsakaninsu da kuma sauran membobin taron. Wang ya kuma jaddada cewa, Sin za ta ci gaba da bin manufofin diplomasiya da shugaba Xi Jinping ya gabatar da ra'ayin tsaro na Asiya, domin karfafa hadin gwiwa da amincewa da juna tsakaninta da bangarori daban daban, da zurfafa hadin gwiwa a duk fannoni, ta yadda za a bude wani sabon babi na tabbatar da zaman lafiya da kwanciyar hankali da samun ci gaba gami da walwala a yankin Asiya da ma duniya baki daya.(Fatima)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China