in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
An kama wanda ya kitsa harin otel Radisson Blu, in ji hukumar tsaron ta Mali
2016-04-23 13:02:48 cri
Jiya Jumma'a 22 ga wata, hukumar tsaron kasar Mali ta fidda rahoto cewa, an kama wanda ya shirya harin ta'addanci da aka kai otel Radisson Blu dake babban birnin kasar, Bamako a ranar 20 ga watan Nuwamba na shekarar 2015.

Haka kuma, bisa rahoton da hukumar ta bayar, an ce, hukumar tsaron kasar ta kama wani wanda ya shirya harin, wani dan kasar Mauritania mai suna Fawwaz Ould ah-Meida, a wata unguwar dake birnin Bamako, sa'an nan, kuma an gano boma-bomai da bindigogi da dama tare da shi.

Daga bisani kuma, hukumar ta bayyana cewa, Fawwaz yana shirya wani hari na daban da zai kai a karshen makon din a birnin Bamako a yayin da aka kama shi.

A kalla mutane 20 ne suka mutu a cikin harin ta'addanci da aka kai otel Radisson Blu, ciki har da 'yan kasar Sin guda 3, an kuma harbe dakaru guda biyu wadanda suka kai hari a otel din. Kuma reshen kungiyar al-Qaeda ta yankin Maghreb ta sanar da daukar alhakin harin na Otel Radisson Blu. (Maryam)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China