in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
An harbe ma'aikatan kiyaye zaman lafiya na MDD a Mali
2016-03-14 10:59:00 cri
Tawagar kiyaye zaman lafiya da MDD dake kasar Mali wato MINUSMA, ta fidda wani rahoto a Lahadin da ta gabata, cewa a kwanan baya ne aka harbe ma'aikatan kiyaye zaman lafiya na MDD biyu, a yayin da suke wani sansani a birnin Tessalit dake arewacin kasar Mali.

Rahoton ya bayyana cewa, da karfe 7 na daren ranar 12 ga wata, wani sojan kiyaye zaman lafiya ya harbe ma'aikatan kiyaye zaman lafiya uku a sansanin, lamarin da ya haddasa rasuwar biyu daga cikinsu nan take, yayin da na ukun ya samu raunuka.

Sai dai an samu nasarar damke wanda ya kai harin, sannan ana ci gaba da gudanar da bincike kan lamarin.

A ranar 25 ga watan Fabrairu, an kaddamar da makamancin wannan harin a wani sansanin MDD dake birnin Kidal a arewa maso gabashin kasar Mali, wani sojan kasar Chadi ya harbi shugaban rundunar, lamarin da ya haddasa rasuwarsa, sannan wani jami'in aikin likita ya rasu sakamakon wannan hari. (Maryam)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China