in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Mai kula da harkokin jin kai na MDD ya nuna gamsuwa da ci gaban da aka samu a Mali
2016-01-23 13:17:54 cri
A karkashin ziyarar aiki tun daga ranar 18 zuwa 22 ga watan Janairu, shugaban ayyukan jin kai na MDD a yankin Sahel, Toby Lanzer, ya ganewa idonsa ci gaban da aka samu da kuma kalubalolin dake wanzuwa a fannonin tsaro da samun hidima ga al'ummomin wadannan yankuna dake fama da rikici, in ji MDD a cikin wata sanarwa.

A yayin wannan rangadi nasa a arewacin kasar da Bamako, mista Lanzer ya gana da mambobin gwamnatin Mali, hukumomin yankuna da kungiyoyin fararen hula da na jin kai. Ya kuma samu damar zuwa biranen Gao da Kidal domin tattaunawa da mutanen da rikicin ya fi shafa tare da ziyartar wasu ayyukan jin kai, in ji wannan sanarwa.

Muhimman ci gaba kamar sake bude makarantu da dama, da kyautatuwar samu ruwan sha da kiwon lafiya, an samu ci gaba sosai kansu. Ci gaban komawar hukumomin gwamnati ya kasance muhimmin abin da ya kamata a tabbatar da kuma karfafa ayyukan ci gaba tare da taimakon kungiyoyin jin kai da ci gaba, in ji mista Lanzer.

A fage, kuma ya lura da kyautatuwar yanayi dalilin sake tura wani bangaren jami'ai a ma'aikatun gwamnati dake muhimmanci da ma goyon bayan kungiyoyin ba da agaji.

Amma duk da haka, wadannan ci gaba da aka samu suna jan kafa a wasu yankuna inda har yanzu ake fuskantar matsalar tsaro dake kuma kawo cikas ga ayyukan yau da kullum, lamarin dake kara tura yawancin al'ummomi cikin mawuyacin hali, in ji sanarwar. (Maman Ada)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China