in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Siasia bai damu ba game da tsara jadawalin wasannin gasar Olympics
2016-04-20 13:10:30 cri
Kociyan 'yan wasan Najeriya 'yan kasa da shekakaru 23 Samson Siasia, ya bayyana cewar tsara jadawalin wasannin kwallon kafa na Rio Olympic wanda 'yan wasan ke rukuni guda da Sweden, da Japan da kuma Colombia ba wata matsala ba ce

An tsara jadawalin wasannin ne a katafaren filin wasa na Maracana a ranar Alhamis din data gabata a Rio de Janeiro, inda tawagar 'yan wasan ta nahiyar Afrika zata buga wasa da kungiyoyin wasannin na Japan daga nahiyar Asiya, da Sweden daga nahiyar turai, sai kasar Colombia daga yankin Amurka a wasannin na Rio.

Da yake jawabi daga Rio de Janeiro bayan tsara jadawalin wasannin, Siasia yace, ba za'a iya cewa kyakkyawa ko mummunan tsari ba ne jadawalin wasannin, kuma yana da kyakkyawar fatar samun nasara a rukunin wasannin da kulub din zai kara. Ya ce baya ga kasancewarta a rukinin B a gasar wasannin, yana fatar Najeriyar zata samu tsallakewa a rukunin wasannin.

Ya ce burin da yake da shi shine na samun lambar girmamawa ta zinare a wasannin na Rio, tun bayan nasarar da kasar ta taba samu na lambar girmamawa ta azurfa a gasar wasanni ta Beijing a 2008, kuma a cewarsa, idan ya koma Najeriya, zai hada kai da sauran masu ruwa da tsaki a harkar wasanni ta kasar don gudanar da shirye shiryen da suka dace, domin cimma wannan nasara.(Ahmad Fagam)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China