in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
'Yan wasan damben kasar Uganda biyu sun samu gurbi a gasar Olympic ta birnin Rio
2016-03-25 19:24:25 cri
'Yan wasan damben kasar Uganda biyu, wato Ronald Serugo, da Kenneth Katende, sun samu gurbi a gasar Olympic dake tafe a birnin Rio na kasar Brazil.

Da yake tsokaci game da hakan, kakakin hukumar wasan damben boksin na kasar ta Uganda Fred Kavuma, ya ce tawagar su, za ta koma gida daga Yaounden kasar Kamaru, bayan fafatawa da suka yi a gasar nahiyar Afirka ta Damben boksin, wadda kwamitin gasar Boksin na kasa da kasa ko AIBA ke shiryawa.

Daya daga 'yan wasan boksin na kasar ta Uganda wato Ronald Serugo, zai yi fita ta biyu ne a gasar Olymphic, bayan ya samu nasara kan abokin karawar sa daga Afirka ta Kudu wato Sikho Nqothol da maki 2 da 1, a rukunin masu matsakaicin nauyi, yayin da shi kuma Katende ya doke Moroke Mokhotho na kasar Lesotho a wasan da suka dambata.

Yanzu haka dai 'yan damben biyu za su bi sahun takwarorin su 9 daga Ugandan, domin fafatawa a gasar Olympic da Brazil za ta karbi bakunci nan gaba cikin wannan shekara.

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China