in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Bolt: Gasar Rio za ta zama Olympics din karshe da zan halarta
2016-03-25 19:25:02 cri

Fitaccen dan wasan tsere na kasar Jamaica Usain Bolt, ya tabbatar da cewa zai yi ritaya bayan halartar gasar Olympics ta wannan shekara, gasar da za ta gudana a birnin Rio de Janeiro na kasar Brazil.

Kafin ya sanar da hakan, Bolt ya ce kocinsa Glen Mills ya shawarce shi da ya ci gaba da halartar wasanni har zuwa shekarar 2020. Amma a nasa bangaren, dan wasan wanda ya taba samun lambobin zinariya guda 6 a wasannin Olympics, ya ce bayan da ya samu nasara a Rio, babu dalilin da zai sa shi ci gaba da halartar wasanni a matsayin koli.

Dan wasan mai shekaru 29 a duniya, ya gaya wa manema labaru cewa, ba shi da cikakkiyar niyyar sake kwashe karin shekaru 4 yana samun horo domin wannan gagarumar gasa wadda ke gudana shekaru hudu-hudu ba.

Bolt ya samu lambobin zinariya a wasannin tsere na mita 100, da mita 200, gami da gudun ba da sanda na mita 400, a wasannin Olympics na London a shekarar 2012, kana ya samu makamantan su a gasar Olympics ta birnin Beijing a shekarar 2008.

A gasar da za ta gudana a watan Agustan bana a Rio, Bolt ya ce yana sa ran kare kambinsa a wadannan wasanni, musamman ma a wasan tsere na mita 200.

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China