in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Ban Ki-moon ya kalubalanci kasar Afirka ta Tsakiya da ta yi zaben raba gardama kan sabon tsarin mulkin kasar cikin lumana
2015-12-13 13:37:26 cri
Babban sakataren MDD Ban Ki-moon ya bayar da sanarwa ta hanyar kakakinsa a ranar 12 ga wata, inda ya kalubalanci bangarori daban daban na kasar Afirka ta Tsakiya da su yi zaben raba gardama kan sabon tsarin mulkin kasar cikin adalci da lumana.

Sanarwar ta bayyana cewa, zaben raba gardama din muhimmin aiki ne wajen kawo karshen lokacin mulkin wucin gadi na kasar Afirka ta Tsakiya, wanda zai aza tubali wajen tabbatar da zaman lafiya a kasar. Ban Ki-moon ya jaddada cewa, MDD na nuna goyon baya ga hukumomin wucin gadi na Afirka ta Tsakiya da su yi kokari wajen aiwatar da ayyuka da yunkurin yin zabe a kasar.

Kasar Afirka ta Tsakiya za ta yi zaben raga gardama kan sabon daftarin tsarin mulkin kasar a ranar 13 ga wata. An ce, bayan makwani biyu, za a yi zaben shugaban kasar da na majalisar dokoki da aka jirkirtar da su sau da dama. (Zainab)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China