in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Ban Ki-moon ya yi kira ga bangarorin Afirka ta Tsakiya da su gudanar da zabe cikin zaman lafiya
2015-12-30 15:55:26 cri
Babban magatakardan MDD Ban Ki-moon ya yi kira ga bangarori daban daban dake kasar Afirka ta Tsakiya da su gudanar da zaben shugaban kasa da na 'yan majalisu da za a gudanar a yau bisa dokoki, zaman lafiya da kuma adalci.

Mr. Ban ya bayyana hakan ne cikin wata sanarwa da ya bayar a jiya Lahadi ta hannun kakakinsa.

Sanarwar ta ce, Ban Ki-moon ya bayyana kwarin gwiwarsa yadda 'yan kasar kimanin miliyan 2 ne suka yi rajista domin kada kuri'u. Don haka, ya bukaci bangarori daban daban na kasar da su hada kai da tawagar musamman ta MDD dake kasar, domin ganin an magance da duk wata matsala da ka iya kawo cikas wajen gudanar da zaben cikin lumana bisa doka.

Bugu da kari, Ban Ki-moon ya nuna yabo ga gwamnatin wucin gadin kasar bisa shirya zaben raba gardama game da kundin tsarin mulkin kasar da ya gudana a farkon watan nan da muke ciki. Ya kuma bayyana cewa, MDD za ta ci gaba da taimaka wa kasar a kokarin da take na tabbatar da zama lafiya da kwanciyar hankali. (Maryam)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China