in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Mutane fiye da dari daya rikicin da ya faru a babban birnin kasar Afirka ta Tsakiya ya shafa
2015-09-30 13:47:08 cri
Firaministan kasar Afirka ta Tsakiya Muhammad Carmon ya bayyana a jiya Talata 29 ga wata cewa, mutane fiye da 20 sun mutu, sannan kuma wadansu kimanin 80 suka ji rauni a sakamakon rikicin da ya faru a Bangui, babban birnin kasar tun daga ranar asabar din da ta wuce.

Mista Carmon ya bayyanawa 'yan jarida ta wayar tarho cewa, ya yi Allah wadai da tada rikicin wanda aka yi shi don hargitsa babban zaben kasar, amma ya tabbatar da cewa, yanzu an samu zaman lafiya a kasar. Firaministan ya yi nuni da cewa, watakila kungiyar dake yunkurin kawo illa ga babban zaben kasar ce ta tada rikicin, domin ta san ba za ta samu ikon mulki ta hanyar zaben ba.

Bayan faruwar rikicin, an yi kira da a gyara jadawalin harkar siyasa a kasar Afirka ta Tsakiya, ciki har da jinkirtar da zaben shugaban kasar da na majalisar dokokin kasar da ake shirin gudanar da su a ranar 18 ga watan Oktoba. Kuma wasu na bukatar da a kada kuri'ar jin ra'ayoyin jama'a game da tsarin mulkin kasar a ranar 4 ga watan Oktoba. (Zainab)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China