in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Zhang Dejiang ya gana da shugaba Buhari
2016-04-13 14:44:28 cri

Shugaban zaunannen kwamitin majalisar wakilan jama'ar kasa ta Sin Zhang Dejiang ya gana da shugaban kasar Nijeriya Muhammadu Buhari a babban dakin taron jama'a dake birnin Beijing a yau Laraba 13 ga wata.

A yayin ganawarsu, Zhang Dejiang ya ce, majalisar wakilan jama'ar kasar Sin tana son kara yin musaya da majalisar dokokin kasar Nijeriya a fannonin dake shafar yaki da cin hanci da shari'a da dai sauransu, domin kyautata dokokin hadin gwiwar tattalin arziki da cinikayya da kuma ciyar da hadin gwiwar hukumomin kafa dokoki na kasashen biyu gaba.

A nasa bangare kuma, shugaba Buhari ya ce, kasar Nijeriya za ta nuna kwazo da himma kan shirye-shiryen bunkasa kasashen Afirka guda goma da ake gudana karkashin taimakon kasar Sin, haka kuma, kasarsa tana son ci gaba da karfafa mu'amala da hadin gwiwar dake tsakanin hukumomin kafa dokoki na kasashen biyu a nan gaba. (Maryam)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China