A Larabar nan ne kakakin ma'aikatar harkokin wajen kasar Sin Lu Kang, ya bayyana cewa shugaban tarayyar Najeriya Muhammadu Buhari, zai gudanar da ziyarar aiki a nan kasar Sin, bisa goron gayyatar da takwaransa na kasar ta Sin Mr. Xi Jinping ya gabatar masa.
Ya ce shugaba Buhari zai ziyarci kasar Sin ne tsakanin ranekun 11 zuwa 15 ga watan nan na Afirilu.(Lubabatu)