Mutanen Sin a Nijeriya na fatan ziyarar shugaba Buhari a Sin za ta inganta dangantakar kasashen biyu
A ran 11 ga wata, shugaban tarayyar Najeriya Muhammadu Buhari ya kai ziyarar aiki a kasar Sin, dangane da wannan ziyara, kamfanonin kasar Sin dake Nijeriya, da wakilan 'yan kasar Sin a Nijeriya sun bayyana kyakkyawan fatansu kan ziyarar shugaba Buhari a kasar Sin a wannan karo, sannan suna sa ran ziyarar za ta kara bunkasa dangantaka dake tsakanin kasashen biyu, a bangare guda ana fatan samun tagomashi game da hadin gwiwar kasashen biyu a fannonin ayyukan noma irin na zamani, da samar da ababen more rayuwa, da ciniki, da sha'anin kudi da dai sauransu. (Maryam)
Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku