in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Gwamnatin Syria na cikin shirin halartar taron neman sulhu na Geneva
2016-04-12 10:43:15 cri
Mataimakin firaminista, kana ministan harkokin wajen kasar Syria Walid Muallem ya bayyana a ran 11 ga wata cewa, gwamnatin kasar za ta halarci taron neman sulhu kan batun Syria a mataki na biyu da za a yi a ran 15 ga watan nan da muke ciki.

Sa'an nan, a yayin da yake ganawa tare da manzon musamman na babban magatakardan MDD kan batun Syria Staffan de Mistura, Mr. Muallem ya bayyana cewa, gwamnatin kasar Syria ba za ta kaucewa halartar wannan taron ba, kana, tana tsayawa tsayin daka wajen yin shawarwarin neman sulhu ba tare da a gindaya wani sharadi ba, kuma ya kamata shawarwarin sun kasance a tsakanin 'yan kasar Syria, haka kuma, 'yan kasar za su ba da jagoranci kan taron.

Kaza lika, ya ce, al'ummomin kasar suna da ikon yanke shawara a kan makomar kasarsu, suna kuma imani cewa, za a iya kawar da kungiyoyin ta'addanci dake kasar, da suka hada da kungiyar IS, reshen kungiyar al-Qaeda na kungiyar AL-Nusra da sauransu.

Staffan de Mistura ya isa birnin Damascus a ran 10 ga wata, sa'an nan ya samu ganawa tare da Mr. Muallem a ran 11 ga wata, inda kafin ya bar kasar ya bayyana wa kafofin watsa labarai cewa, babban makasudin ziyararsa a wannan karo shi ne, tattaunawa tare da Mr. Muallem kan ayyukan shirye shiryen taron neman sulhu, haka kuma, sun tattauna kan muhimmancin yarjejeniyar tsagaita bude wuta. (Maryam)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China