in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Gwamnatin kasar Syria za ta halarci shawarwarin shimfida zaman lafiya bayan kammala zaben majalisar dokokinta
2016-04-06 10:52:17 cri
Mataimakin ministan harkokin wajen kasar Syria Faisal Mekdad ya bayyana a ranar 5 ga wata cewa, tawagar gwamnatin kasar Syria za ta tashi zuwa birnin Geneva don halartar shawarwarin shimfida zaman lafiya bayan da aka gama zaben majalisar dokokin kasar a wannan wata.

Gidan telebijin na pan-Arab al-Mayadeen ya ruwaito kalaman mista Mekdad na cewa, kasar Syria za ta tabbatar da ikon mallaka da 'yancin kan kasar, tilas ne bangarori daban daban su girmama ra'ayin jama'ar kasar Syria.

An kammala shawarwarin shimfida zaman lafiya kan batun Syria na sabon zagaye a ranar 24 ga watan Maris na bana, a yayin shawarwarin na tsawon kwanaki kwanaki 10, gwamnatin kasar Syria da kwamitin yin shawarwari na kungiyoyin masu adawa sun cimma daidaito kan batutuwa 12. Manzon musamman na babban sakataren MDD mai kula da batun Syria Staffan de Mistura ya sanar cewa za a bude sabon zagayen shawarwarin a ranar 9 ga watan Afrilu.

Shugaban kasar Syria Bachar al Assad ya ba da umurni a watan Febrairu cewa, za a gudanar da majalisar dokokin jama'ar kasar a ranar 13 ga watan Afrilu. (Zainab)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China