in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Wasu jama'ar kasar Syria sun koma biranen da IS ta taba mamaye a baya
2016-04-10 13:10:22 cri
Wani jami'in kasar Syria ya bayyana a jiya Asabar ranar 9 ga wata cewa, sojojin gwamnatin kasar sun riga sun kwace biranen Palmyra, da Gallatin dake tsakiyar kasar, kuma tun daga ranar jama'ar kasar kimanin 2000 sun soma komawa garuruwansu.

Kamfanin dillancin labarum kasar Syria ya ruwaito maganar shugaban lardin Homs dake tsakiya kasar na cewa, wadannan jama'a sun tashi daga Homs zuwa Palmyra da Gallatin cikin motocin safa safa sama da 40. Kafin haka dai kwararru sun riga sun isa biranen biyu, don kawar da nakiyoyin da 'yan kungiyar IS suka dasa kan hanyoyi, an kimanta cewa, za a farfado da aikin jinya, da ayyukan samar da wutar lantarki, da ruwa da dai sauransu a cikin 'yan makwanni masu zuwa.

Biranen Palmyra da Gallatin suna kudu maso gabashin birnin Homs. Kungiyar IS ta kai hari kan wadannan birane biyu a watannin Mayu da Agustan bara, hakan ya tilastawa fararen hula da dama tserewa daga gidajensu. A karshen watan Maris da farkon wannan watan, sojojin gwamnatin kasar tare da taimakon sojojin kasar Rasha sun kwato wadannan biranen biyu.

Bisa kididdigar da MDD ta yi an nuna cewa, tun bayan barkewar rikicin Syria a shekarar 2011 har zuwa yanzu, mutane dubu 250 suka rasa rayukansu, yayin da miliyan 6.5 suka rasa gidajensu. (Bilkisu)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China