Hukumar zabe mai zaman kanta ta kasar ta fidda labarin cewa, adadin masu jefa kuri'u da suka yi rajista ya kai miliyan 6, wadanda suka kada kuri'u a rumfunan zabe dake wurare daban daban a wannan rana. Haka kuma, hukumar ta bayyana cewa, za a gabatar da sakamakon zaben bayan makwanni biyu, kana, idan babu wanda ya samun kuri'u na kashi 50 bisa dari, za a je zaben shugaban kasar zagaye na biyu.
Idriss Deby ya kafa jam'iyyar tabbatar da kishin kasa a watan Maris na shekarar 1990, ya kuma kasance shugaban jam'iyyar, sa'an nan, a watan Disamba na shekarar 1990 ya hau kujerar shugaban kwamitin harkokin kasar Chadi. Daga bisani kuma, a watan Maris na shekarar 1991, ya zama shugaban kasar Chadi, inda ya kuma ci gaba da lashe babban zaben shugaban kasar har sau duhu a shekara ta 1996, 2001, 2006 da kuma shekarar 2011. (Maryam)