Mista Sylla Bakari ya yi kira ga dukkan 'yan kasar Chadi baki daya da su fito kwansu da kwalkwata domin tarbon sojojin da suka kammala aikinsu. A ranar 7 ga watan Nuwamba, sojojin Chadi da aka tura a kasar Kamaru, bisa irin wannan dalili na yaki da Boko Haram, an yi musu babban tarbo a matsayin manyan jaruman kasa a birnin N'Djamena. (Maman Ada)