Ana sa ran ganin jama'ar kasar fiye da miliyan 6.2 wadanda suke cikin kasar ko kuma a ketare, zasu kada kuri'a domin zaben daya daga cikin 'yan takara 14 dake neman kujerar shugabancin kasar.
Shugaban kasar mai ci Idriss Deby Itno ya kwashe shekaru 25 yana mulkin wannan kasa dake yammacin Afrika, sa'an nan a wannan karo zai nemi samun wa'adin aikinsa na 5.
Sauran abokan hamayyar shugaba Deby sun hada da shugaban 'yan adawa Saleh Kebzabo da tsohon firaminista Joseph Djimrangar Dadnadji.(Bello Wang)