in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
MDD ta yi Allah wadai da harin Boko Haram a tsibirin tafkin Chadi
2015-12-07 09:56:33 cri
Babbabn Sakataren MDD Ban Ki-moon, a ranar Lahadin nan, ya yi Allah wadai da wasu tagwayen hare haren kunar bakin wanda mayakan Boko Haran masu ikirarin kishin Islama suka kai a tsibirin Koulfoua na kasar Chadi dake daura da tafkin Chadi.

A jiya Lahadi wasu mahara 4, suka tada boma bomai a tsribirin na Koulfoua, lamarin da ya yi sanadiyyar mutuwar su nan take da wasu mutane 19, sannan harin ya raunata mutane 130.

Sanarwar ta mista Ban, ta bayyna harin a matsayin kisan rashin imani da kungiyar Boko Haram ke kaddamarwa.

Ban, ya bukaci kasashen da matsalar Boko Haram ta shafa, dasu binciko musabbabin bullar rikicin don daukar matakan kawo karsen sa.

Yankin gabar tafkin Chadi yana fama da hare haren kungiyar Boko Haram, lamarin da ya tilasta gwamnatin kasar Chadi kafa dokar tabaci a yankin mai makwataka da Kamaru, Nijer da kuma Najeriya.

A ranar 18 ga watan Nuwamba ne, majalisar dokokin kasar Chadi ta sake tsawaita wa'adin dokar tabacin zuwa watanni 4.(Ahmad Fagam)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China